Quran Apps in many lanuages:

Surah Ash-Shu'ara Ayahs #161 Translated in Hausa

فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُمْ مُؤْمِنِينَ
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ الْمُرْسَلِينَ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Choose other languages: