Quran Apps in many lanuages:

Surah Ash-Shu'ara Ayahs #120 Translated in Hausa

قَالُوا لَئِنْ لَمْ تَنْتَهِ يَا نُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَ
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِي وَمَنْ مَعِيَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
فَأَنْجَيْنَاهُ وَمَنْ مَعَهُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

Choose other languages: