Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Qalam Ayahs #21 Translated in Hausa

إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
وَلَا يَسْتَثْنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِنْ رَبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
فَتَنَادَوْا مُصْبِحِينَ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

Choose other languages: