Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Qalam Ayahs #20 Translated in Hausa

سَنَسِمُهُ عَلَى الْخُرْطُومِ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
إِنَّا بَلَوْنَاهُمْ كَمَا بَلَوْنَا أَصْحَابَ الْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
وَلَا يَسْتَثْنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
فَطَافَ عَلَيْهَا طَائِفٌ مِنْ رَبِّكَ وَهُمْ نَائِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
فَأَصْبَحَتْ كَالصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

Choose other languages: