Quran Apps in many lanuages:

Surah Ta-Ha Ayahs #11 Translated in Hausa

وَإِنْ تَجْهَرْ بِالْقَوْلِ فَإِنَّهُ يَعْلَمُ السِّرَّ وَأَخْفَى
Kuma idan ka bayyana da magana, to, lalle Shi, Yanã sanin asĩri da mafi bõyuwa.
اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ۖ لَهُ الْأَسْمَاءُ الْحُسْنَىٰ
Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau.
وَهَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىٰ
Kuma shin, lãbarin Mũsã yãje maka?
إِذْ رَأَىٰ نَارًا فَقَالَ لِأَهْلِهِ امْكُثُوا إِنِّي آنَسْتُ نَارًا لَعَلِّي آتِيكُمْ مِنْهَا بِقَبَسٍ أَوْ أَجِدُ عَلَى النَّارِ هُدًى
A lõkacin da ya ga wata wuta, sai ya ce wa iyãlinsa, "Ku dãkata. Lalle ne nĩ, na tsinkãyi wata wuta tsammãnĩna in zo mukuda makãmashi daga gare ta, kõ kuwa in sãmi wata shiriya a kan wutar."
فَلَمَّا أَتَاهَا نُودِيَ يَا مُوسَىٰ
Sa'an nan a lõkacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Mũsã!"

Choose other languages: