Quran Apps in many lanuages:

Surah As-Saaffat Ayahs #40 Translated in Hausa

وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَجْنُونٍ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنْتُمْ تَعْمَلُونَ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Choose other languages: