Quran Apps in many lanuages:

Surah As-Saaffat Ayahs #152 Translated in Hausa

فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
أَلَا إِنَّهُمْ مِنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

Choose other languages: