Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Mumenoon Ayahs #7 Translated in Hausa

وَالَّذِينَ هُمْ عَنِ اللَّغْوِ مُعْرِضُونَ
Kuma waɗanda suke, sũdaga barin yasassar magana, mãsu kau da kai ne.
وَالَّذِينَ هُمْ لِلزَّكَاةِ فَاعِلُونَ
Kuma waɗanda suke ga zakka mãsu aikatãwa ne.
وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَ
Kuma waɗanda suke ga farjõjinsu mãsu tsarẽwa ne.
إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
Fãce a kan mãtan aurensu, kõ kuwa abin da hannayen dãmansu suka mallaka to lalle sũ bã waɗanda ake zargi, ba, ne.
فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ
Sabõda haka wanda ya nẽmi abin da ke bãyan wancan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙẽtarẽwar haddi.

Choose other languages: