Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Insan Ayahs #20 Translated in Hausa

قَوَارِيرَ مِنْ فِضَّةٍ قَدَّرُوهَا تَقْدِيرًا
¡arau na azurfa, sun ƙaddara su ƙaddarawa, daidai bukãta.
وَيُسْقَوْنَ فِيهَا كَأْسًا كَانَ مِزَاجُهَا زَنْجَبِيلًا
Ana shayarwa da su, a cikinta, finjalan giya, wadda abin gaurayarta ya kasance zanjabil ne.
عَيْنًا فِيهَا تُسَمَّىٰ سَلْسَبِيلًا
Wani marmaro ne, a cikinta, ana kiran sa salsabil.
وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَانٌ مُخَلَّدُونَ إِذَا رَأَيْتَهُمْ حَسِبْتَهُمْ لُؤْلُؤًا مَنْثُورًا
Kuma wasu yara samãrin dindindin na kẽwayãwa, a kansu, idan ka gan su, zã ka zaci sũ lu'ulu'u ne wanda aka wãtsa.
وَإِذَا رَأَيْتَ ثَمَّ رَأَيْتَ نَعِيمًا وَمُلْكًا كَبِيرًا
Kuma idan kã ga wannan wurin, to, kã ga wata irin ni'ima da mulki babba.

Choose other languages: