Quran Apps in many lanuages:

Surah Ta-Ha Ayahs #21 Translated in Hausa

وَمَا تِلْكَ بِيَمِينِكَ يَا مُوسَىٰ
"Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!"
قَالَ هِيَ عَصَايَ أَتَوَكَّأُ عَلَيْهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِي وَلِيَ فِيهَا مَآرِبُ أُخْرَىٰ
Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshẽna kuma inã da waɗansu bukãtõci na dabam a gare ta."
قَالَ أَلْقِهَا يَا مُوسَىٰ
Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!"
فَأَلْقَاهَا فَإِذَا هِيَ حَيَّةٌ تَسْعَىٰ
Sai ya jẽfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa.
قَالَ خُذْهَا وَلَا تَخَفْ ۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا الْأُولَىٰ
Ya ce: "Ka kãma ta kuma kada ka ji tsõro. Za Mu mayar da ita ga hãlinta na farko."

Choose other languages: