Quran Apps in many lanuages:

Surah Ash-Shu'ara Ayahs #25 Translated in Hausa

فَفَرَرْتُ مِنْكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْمًا وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَ
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدْتَ بَنِي إِسْرَائِيلَ
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِنْ كُنْتُمْ مُوقِنِينَ
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ أَلَا تَسْتَمِعُونَ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

Choose other languages: