Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Qamar Ayahs #21 Translated in Hausa

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِنْ مُدَّكِرٍ
Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ عَادٌ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًا صَرْصَرًا فِي يَوْمِ نَحْسٍ مُسْتَمِرٍّ
Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
تَنْزِعُ النَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ مُنْقَعِرٍ
Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?

Choose other languages: