Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Qalam Ayahs #29 Translated in Hausa

وَغَدَوْا عَلَىٰ حَرْدٍ قَادِرِينَ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوا إِنَّا لَضَالُّونَ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُلْ لَكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
قَالُوا سُبْحَانَ رَبِّنَا إِنَّا كُنَّا ظَالِمِينَ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

Choose other languages: