Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Haaqqa Ayahs #7 Translated in Hausa

وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِ
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِ
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

Choose other languages: