Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Haaqqa Ayahs #21 Translated in Hausa

وَالْمَلَكُ عَلَىٰ أَرْجَائِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌ
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنْكُمْ خَافِيَةٌ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَءُوا كِتَابِيَهْ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
إِنِّي ظَنَنْتُ أَنِّي مُلَاقٍ حِسَابِيَهْ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَاضِيَةٍ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

Choose other languages: