Quran Apps in many lanuages:

Surah At-Tur Ayahs #17 Translated in Hausa

يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
هَٰذِهِ النَّارُ الَّتِي كُنْتُمْ بِهَا تُكَذِّبُونَ
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
أَفَسِحْرٌ هَٰذَا أَمْ أَنْتُمْ لَا تُبْصِرُونَ
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
اصْلَوْهَا فَاصْبِرُوا أَوْ لَا تَصْبِرُوا سَوَاءٌ عَلَيْكُمْ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنْتُمْ تَعْمَلُونَ
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَنَعِيمٍ
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.

Choose other languages: