Quran Apps in many lanuages:

Surah Ash-Shu'ara Ayahs #75 Translated in Hausa

قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
أَوْ يَنْفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
قَالَ أَفَرَأَيْتُمْ مَا كُنْتُمْ تَعْبُدُونَ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

Choose other languages: