Quran Apps in many lanuages:

Surah Ash-Shu'ara Ayahs #50 Translated in Hausa

فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
رَبِّ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
قَالَ آمَنْتُمْ لَهُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُمْ مِنْ خِلَافٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
قَالُوا لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا مُنْقَلِبُونَ
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

Choose other languages: