Quran Apps in many lanuages:

Surah As-Saaffat Ayahs #70 Translated in Hausa

فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِنْ حَمِيمٍ
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

Choose other languages: