Quran Apps in many lanuages:

Surah As-Saaffat Ayahs #32 Translated in Hausa

قَالُوا إِنَّكُمْ كُنْتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
قَالُوا بَلْ لَمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُمْ مِنْ سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنْتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

Choose other languages: