Quran Apps in many lanuages:

Surah Al-Qalam Ayahs #37 Translated in Hausa

كَذَٰلِكَ الْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ الْآخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا يَعْلَمُونَ
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِنْدَ رَبِّهِمْ جَنَّاتِ النَّعِيمِ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
أَفَنَجْعَلُ الْمُسْلِمِينَ كَالْمُجْرِمِينَ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
أَمْ لَكُمْ كِتَابٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

Choose other languages: